Ilimi Hasken Rayuwa

  • Autor: Vários
  • Narrador: Vários
  • Editora: Podcast
  • Duração: 3:57:54
  • Mais informações

Informações:

Sinopse

Wannan Shirin ya shafi Fadakar da al'umma game da ci gaban da aka samu a sha'anin Ilimi a fannoni daban-dabam a duniya, tare da nazari ga irin ci gaban da aka cim ma wajen binciken kimiya da fasaha da ke naman saukakawa Danadam wajen tafiyar da rayuwarsa a duniya. Shirin kuma zai yi kokarin jin irin bincike da masana ke yi domin inganta rayuwar Biladam. Shirin na zo maku ne, a duk ranar Talata a shirye-shiryenmu na safe.

Episódios

  • Ra'ayoyi sun banbanta kan amfani da fasahar AI wajen yin tiyata

    24/02/2026 Duração: 10min

    Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako a wannan makon, ya mayar da hankali kan binciken da ya gano cewa shigar fasahar AI cikin fannin tiyata na haifar da wasu matsaloli masu kama da barazana ga rayuwar ɗan adam, kan haka ne ma muka zanta da masana a fannin kimiyya da kuma ɓangaren lafiya, inda muka jiyo ra’ayoyin mutane game da yadda wasu ke yarda AI ya duba lafiyarsu har ta kai ga tiyata a wasu lokutan. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna............

  • Yadda satar jarabawa ke taka rawa wajen kassara ingancin ilimi a Najeriya

    17/02/2026 Duração: 10min

    Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali kan yadda satar jarabawa ke ƙoƙarin zama ruwan dare a makarantun sassan Najeriya, matsalar da ke ci gaba da illa ga ingancin ilimi a dukkan makarantu na ƙasar. Akwai zarge-zargen da ke nuna cewa wasu daga cikin jami'an hukumomin da ke kula da shirya jarabawa a matakai daban-daban na taimakawa wannan mummunar ɗabi'a ta satar jarabawa ta hanyar fallasa amsoshin tambayoyin da ake shirin fitarwa ga ɗalibai. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

  • Yadda masu larurar ji ke fama da ƙalubalen karatu a Najeriya

    10/02/2026 Duração: 09min

    Shirin na wannan mako ya ba da hankali ne akan yadda masu fama da larurar ji ke fama da ƙalubalen karatu a wasu sassan Najeriya.

  • Ana fuskantar koma bayan koyan harshen larabci a arewacin Najeriya

    03/02/2026 Duração: 09min

    Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan mako tare da Shamsiyya Haruna ya mayar da hankali ne kan dalilan da suka haddasa rashin koyon ingantaccen larabci tsakanin daliban sakandare a arewacin Najeriya, sabanin lokutan baya. A shekarun baya, alkaluma sun nuna cewa kusan kaso hamsin na larabcin da Dalibai ke koya suna samun sa ne a makarantun boko ba lallai sun sun halarci makarantun Arabiya, al’amarin dake neman zama tarihi a wannan zamani. Shiga alamar sauti don sauraron cikakken shirin.......

  • Yadda satar jarabawa da cin hanci da rashawa ke kassara ɓangaren Ilimi a Kamaru

    27/01/2026 Duração: 09min

    Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali ne kan yadda wani bincike can a Jamhuriyyar Kamaru ya gano yadda satar Jarabawa da cin hanci da rashawa ke mummunan tasiri a ɓangare ilimin ƙasar. Matsalar ta cin hanci da rashawa kai tsaye ta yi mummunar illa ga yanayin ɗaukar malamai aiki da gina makarantu ko kuma samar da ci gaba a ɓangaren na Ilimi, yayinda a gefe guda satar jarabawar da ɗalibai ke yi ke zagon ƙasa ga makomar ilimi a ƙasar. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

  • Makomar karatu a yankin arewacin Najeriya cike da barazanar ƴanbindiga

    20/01/2026 Duração: 09min

    Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan mako tare da Shamsiyya Haruna ya mayar da hankali kan makomar karatun ɗalibai a makarantun Najeriya musamman yankin arewaci mai fama da matsalolin tsaro, dai dai lokacin da aka koma sabon zangon karatu Iyaye na cike da fargaba kan tsaro a makarantu. Makwanni gabanin tafiya hutun zangon da ya gabata cikin watan Nuwamban bara ne, hare-haren ƴan bindiga suka tilasta kulle makarantu a sassan arewacin Najeriyar ciki har da makarantun Unity da ke ƙarƙashin kulawar gwamnatin Tarayya. Wasu na da ra'ayin cewa sai an haɗa ƙarfi da ƙarfe tsakanin dukkanin ɓangarori ne, ɗalibai za su samu cikakken tsaro a makarantu tare da samun ɗorewar Ilimi a yankin. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin.

  • Kashi na biyu kan yadda sabuwar manhajar fassarawa da lissafa haraji ke amfani a Najeriya

    06/01/2026 Duração: 09min

    A kashi biyu na shirin ilimi hasken rayuwa, mun ɗora kan sabuwar manhajar fassarawa da da sauƙaƙa lissafin karɓar haraji. Ku danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Faruk Yabo.

  • Farfesa Aminu Bello ya samar da manhaja mai sauƙaƙa lissafin haraji a Najeriya

    30/12/2025 Duração: 09min

    Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon ya tattauna da Farfesa Aminu Bello Usman daga  Birtaniya, ɗan jihar Kano da ke tarayyar Najeriya, wanda ya ƙirƙiri wata Manhaja da za ta taimaka wa mutane wajen sauƙaƙa musu lisaffin hada-hadar kuɗaɗe musamman ma na haraji. Wani abin ban sha’awa dangane da Manhajar da aka fi sani da Software a Turance, shi ne yadda wannan manhajar ta ƙunshi harsuna biyar. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nasir Sani.

  • Akwai bukatar samarwa masu buƙata ta musamman ayyukan yi domin dogaro da kai

    23/12/2025 Duração: 09min

    Mutane da suka tsinci kansu a cikin masu buƙata ta musamman sakamakon nau’ikan nakasar da suka fama da ita sun share shekaru suna fuskantar giɓi babba a muhimman fannonin rayuwa daban daban, ciki kuwa har da samun guraben ayyukan yi ko da kuwa a ce sun yi katarin tsallake shingen samun ilimi, matsalar da ta fi ƙamari a ƙasashe masu tasowa ciki har da na Nahiyar Afrika. Mutane da suka tsinci kansu a cikin masu buƙata ta musamman sakamakon nau’ikan nakasar da suka fama da ita sun share shekaru suna fuskantar giɓi babba a muhimman fannonin rayuwa daban daban, ciki kuwa har da samun guraben ayyukan yi ko da kuwa a ce sun yi katarin tsallake shingen samun ilimi, matsalar da ta fi ƙamari a ƙasashe masu tasowa ciki har da na Nahiyar Afrika. Kan wannan batu shirin Ilimi Hasken rayuwa na wannan lokaci zai tattauna, bayan da ya yi tattaki zuwa Jihar Jigawa da ke tarayyar Najeriya, akan ƙorafin da wasu fama da nakasar suka yi a bisa ganin cewar suna neman rasa damar samun guraben ayyukan yi da suka cancanci dafewa.   A

  • Makarantu a Kano sun fara kai ƙarar iyayen yara sabida bashin kuɗin makaranta

    09/12/2025 Duração: 09min

    Shirin ilimi Hasken rayuwa na wannan mako dubi ne kan yadda makarantu masu zaman kan a jihar Kano da ke Arewacin Najeriya, suka fara ɗaukar matakin kai ƙarar iyayen yara gaban hukumomi, sakamakon rashin biyansu kuɗaɗen karatun ƴaƴansu na tsawon lokaci. Abin damuwar shine, idan iyayen suka tara kuɗin makaranta har ya kai matakin da ba za su iya biya ba, sai su sauya wa yaran nasu wurin makarantu, kenan wancan kuɗi da ake binsu ya bi ruwa. Babbar matsalar ita ce, wannan al’amari a wasu lokutan ya kan haifar da ƙalubale ga ɓangarorin da ke gudanar da irin wadannan makarantu, abin da har ke kaiwa ga rufewa ko kuma sayar da makaranta, saboda rashin isassun kuɗin da za su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna..........

  • Rashin albashi na shafar aikin koyarwa a makarantu masu zaman kansu a Najeriya - Rahoto

    02/12/2025 Duração: 10min

    A wannan makon, shirin yayi dubi ne kan batun yadda har kawo yanzu ake samun malaman makaratu masu zaman kansu a Najeriya dake ɗaukar albashin Naira dubu 15 zuwa sama, maimakon mafi ƙaranci albashin naira dubu 70 da gwamnati ƙasar ta yi dokar biya. Duk da irin kuɗaden da ake shatawa iyayen yara, har ta kai idan yaronka ba a biya mishi kuɗin makaranta ba, to kuwa za a kora maka shi gida, hakan be sanya sun inganta albashin malaman ba. Makaranta mai zaman kanta mutum ke kafa ta ko haɗin gwiwa na wasu mutane domin taimakawa ko ba gudunmawa yayin da a wannan lokaci da dama sun mayar da ita matsayin kasuwanci, abin da masana ke ganin kenan akwai buƙatar Malamai su samu yanayi mai kyau da walwala wanda ta hakanne zasu samu ƙwarin gwiwa wajan bayar da ilimi mai nagarta. Hauwa'u Adam dake koyarwa a wata Makarata dake yankin Jambulo a jihar Kanon Najeriya, ta sheda mana cewa saboda karatunta yakai matakin digiri ne ake biyanta Naira dubu 20, amma masu kwalin babbar difloma ta HND da NCE albashin daga dubu 17 ne zuwa 1

  • Makomar ilimi dalilin rufe makarantu sabida matsalar tsaro a Najeriya

    25/11/2025 Duração: 10min

    A wannan makon shirin ya karkata akala ne kan makomar ilimi a Najeriya, inda hukumomi suka fara rufe makarantu saboda matsalolin tsaro da ke neman dakushe makomar ilimin manyan gobe. Me yasa jihohi ke gaggawar rufe makarantu bayan sace ɗalibai a Kebbi da Niger a kwanan nan? Shin babu wasu hanyoyin kawo ƙarshen matsalar tsaro sai dai rufe makarantu?   Tambayar kenan da ‘yan Najeriya ke yiwa gwamnatin ƙasar, yayin da ake ganin tarin jami’an tsaro na yiwa masu rike da manyan makamai rakiya, abin da ke nuna yawan jami’an tsaron da ƙasar ke da shi idan aka haɗa ƴansanda da sojoji da jami’an tsaron Civil Defence da sauransu, to kuwa iyaye suka ce idan har aka yi la’akari da wannan za a iya samarwa ɗalibai tsaro. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna.........

  • Har yanzu Malama tsangaya na amfani da Ajami wajen musayar sakonni

    11/11/2025 Duração: 09min

    Shirin a wannan mako, kareshe ne kan maudu’in da muka tattaunawa a makonni biyun da suka gabata, wanda ya mayar da hankali kan yadda rubutun Ajami a kasar Hausa ya yi shura, da kuma yadda yake neman bacewa a wannan zamani. Yayin da ake ganin har yanzu a Jamhuriyar Nijar, akwai yankunan da suke amfani da ajami wajen isar da sakonni, Malaman tsangaya daga Najeriya ma suna amfani da wannan tsarin rubutu wajen musayar bayanai a tsakaninsu. Yaɗuwar addinin Islama a Ƙasar Hausa masana suka ce, ya taimaka sosai wajen shaharar wannan salo na rubutu, sannan kuma ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen inganta hanyoyin sadarwa na wancan lokaci. A tattaunawarmu da masanin tarihi daga Kanon Najeriya, farfesa Tijjani Naniya, ya bayyana cewa, zuwan turawan mulkin mallaka, shine musabbabin gushewar wannan rubutu a kasar Hausa, amma a wancan lokaci, rubutun na ajami ya ci kasuwa tsakanin masana, malamai, sarakuna da kuma ‘yan kasuwa.

  • Tasirin rubutun Ajami wajen musayar bayanai tsakanin al'ummar Hausawa ( 2)

    04/11/2025 Duração: 10min

    Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya cigaba ne da mayar da hankali kan makomar rubutun Ajami a ƙasar Hausa, nau'in rubutun da ya taimaka matuƙa wajen musayar bayanai tsakanin al'ummar Hausawa tun gabanin zuwan Turawan mulkin mallaka.     A shekarun baya-bayan nan rubutun na Ajami ya zama tarihi a ƙasar Hausa bayan da kowanne ɓangare ya rungumi tsarin boko daga turawan Yamma. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin kashi na biyu:

  • Tasirin rubutun Ajami wajen musayar bayanai tsakanin al'ummar Hausawa

    28/10/2025 Duração: 09min

    Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali kan makomar rubutun Ajami a ƙasar Hausa, nau'in rubutun da ya taimaka matuƙa wajen musayar bayanai tsakanin al'ummar Hausawa tun gabanin zuwan Turawan mulkin mallaka. A shekarun baya-bayan nan rubutun na Ajami ya zama tarihi a ƙasar Hausa bayan da kowanne ɓangare ya rungumi tsarin boko daga turawan Yamma. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.....

  • Yadda dokar rage kuɗin makaranta za ta yi tasiri ga tsarin Ilimi a Nijar

    14/10/2025 Duração: 10min

    Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali ne kan dokar da ta tilastawa makarantu masu zaman kansu rage kudin makaranta da gwamnatin Nijar ta kafa, wanda ke zuwa bayan ƙarin hutun makarantu na makwanni biyu saboda mamakon ruwan a ƙasar ta yankin Sahel. Ƙarƙashin wata doka da shugaban gwamnatin Sojin Nijar Abdourraham Tchiani ya sanya hannu ce ta buƙaci dukkanin makarantun su rage kuɗin da suke karɓa da kashi 20, kodayake wannan doka bata shafi makarantun da ke karɓar kuɗin da bai kai CFA jaka hamsin ba. Tuni iyaye suka yi maraba da wannan mataki. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.

  • Malamai a Najeriya na fuskantar tarin matsaloli saboda rashin kyawun albashi

    07/10/2025 Duração: 10min

    Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan makon ya mayar da hankali kan gudunmawar malaman makaranta ga rayuwar jama'a dai dai lokacin da aka gudanar da bikin ranar Malamai a sassa daban-daban na duniya. Majalisar Ɗinkin Duniya ce ta ware wannan rana da nufin girmama gudunmawar da malaman ke bayarwa, sai dai an gudanar da wannan rana ne a dai dai lokacin da malamai a Najeriya dama sauran ƙsashen Afrika ke ganin ƙololuwar matsin rayuw sakamakon matsalolin da suka dabaibaye su kama daga rashin kyawun yanayin aiki dama ƙarancin albashi. Ku latsa alamar sauti don sauraren cikakken shirin...

  • Yadda aikin gona ke hana dimɓin yara zuwa makaranta a Najeriya

    30/09/2025 Duração: 09min

    Shirin ilimi hasken rayuwa na wannan mako ya duba yadda wasu manoma a Najeriya, musamman arewacin kasar ke hana yaransu zuwa makaranta, har sai an yi girbin amfanin gona, saboda wasu dalilai Ku shiga alamar sauti domin sauraron cikakken shirin.....

  • Yadda bikin kammala karatu ke taka rawa wajen lalata tarbiyyar Ɗalibai

    23/09/2025 Duração: 09min

    Shirin Ilimi Hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali ne kan yadda bikin yaye ɗalibai da ɗabi'ar rubutu a jikin rigunan juna dama sauran shagulgulan da akanyi a bikin na kammala makaranta ke taka muhimmiyar rawa wajen lalata tarbiyyar ɗalibai. Tsawon shekaru aka ɗauka wannan dabi'a na ciwa iyaye tuwo a ƙwarya dama sauran masu ruwa da tsaki a ɓangaren tarbiyyar al'umma. Sai dai bayan tsanantar ƙorafe-ƙorafe kan wannan ta'ada, kwatsam an wayi gari gwamnatin jihar Kaduna ta yi uwa da makarɓiya wajen haramta irin bukukuwan har ma da wasu ƙarin dokoki da suka shafi sashen na ilimi ciki har da haramtawa makarantu ƙarin kuɗin makaranta. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna.

  • Yadda ake fama da ƙarancin malamai a makarantun jihar Jigawa ta Najeriya

    16/09/2025 Duração: 09min

    Shirin na wannan rana zai ɗora kan wanda muka gabatar muku a makon jiya game da karancin malamai a makarantun jihar Jigawa ta arewacin Najeriya. Danna alamar saurare domin jin cikakken shirin tare da Nura Ado Sulaiman.

página 1 de 2